Return to BahaiPrayers.net
Facebook
Igiyar dake ɗaure zūkāce yanda ya kamāta, ita cē, biyayya. Idan sun haɗu, yā cancanta masōyā, su gwadāwa jūna amānā matuƙa.
Kada ku yarda kīshi, ya shiga tsakāninku, sabōda kīshi, kamar gubā, yana gurɓāta tūshen sōyayya.
Kada ku yarda, matsalōlin yau da kullun, da hālin zaman yau da gōbe dake sauyāwa kōwace rānā, su zama dalīlin rabuwarku.
Idan tāshin hankali ya ɓullo, ku tattauna tsakāninku, sabōda tsōron kada waɗansu, su maida ƙwāyar ƙasa ta zama babban dūtsi.
Zūkācenku, su zama kamar madūbai biyu, dake gwada ƙyalƙyalin taurārun samāniyar sōyayya da shāwa.
Martabarku da īmāninku, su zama sū nē abun zancenku. Kada ku ɓōyēwa jūna kōmi. Gidanku, ya zama mafaƙar hūtū da konciyar hankali.
Ku karɓi kōwā. Ku būde ƙōfarku ga aminnai kō ɓāki. Ku karɓi maziyartanku da marhaba cikin shinfiɗar huska. Duk wanda ya zō gidanku, ya jī kamar yā zō gidansa nē.
Gidanku, ya zama tamkar aljanna, duk wanda ya shiga, ya ga tūshen ƙāyatarwa, kuma ya yi kirārin cēwa, « gā gidan sōyayya ! Gā fādar sōyayya ! gā gidan tsuntsāyen sōyayya ! gā garkar sōyayya!»
Idan Allah Subahānahu wa ta āla ya bā ku yāra nagari, ku ɗauki nauyin bā su tarbiyya, kuma ku jāgōrancē su, har su zamana furanni da bā su yaushi, cikin lambun wardin Ubangiji, su zama tsuntsāyen aljanna, su zama māsu kyautatāwa al’umma, a taƙaice dai, su zama sū nē ƴāƴan itāciyar rāyuwarku.
Ku zamēwa jūna, tamkar masōyan samāniya, kuma gātāyen Ubangiji, dake zaune cikin aljannar sōyayya.
Ku gina mabartarku bisa rēshen iccen sōyayya.
Ku yi tafiya cikin garkar wardi maras ƙārēwa ta sōyayya.
Ku tsaya tsayin daka, bisa hanyar sōyayya.
Ku shinshina ƙamshin furannin sōyayya.
Gūrinku, ya ƙunshi karāmar abincin sōyayya, kuma batūtuwanku, su zama tamkar jērin farāren lu’u’lu’un tēkun sōyayya.
Ku shā matuƙa, ruwan sōyayya, sabōda ku rāyu har kullun cikin ƙaunar Allah Ubangiji.
- `Abdu'l-Bahá