Return to BahaiPrayers.net
Facebook
Shīnē Sarki, Masani, Mai hikima ! Ka saurāri sūdar aljanna dake bisa rassun itāciyar dawwama har abada. Tana rēra tsarkakakkiyar wāƙa mai dāɗi, tana ayyanāwa rāyuka na gari, bushārar kusantaka da Allah. Tana gayyatar waɗanda suka bāda gaskiya da kaɗaitakar Allah, su isō dandalin mayalwaci. Tana gayāwa waɗanda ba su sarƙafu da abun dūniya ba, sāƙon da ya sauko daga Allah sarki, maɗaukaki, da bā shi abōkin tārayya. Tana jāgōrar mumunai zuwa wajen gadon tsarkaka, kuma wajen wannan nagartacen kyāwo.
A gaskiya, gā kyāwo mafīfīci, wanda aka ambata cikin littatafan manzonni, wanda ya zō dōmin ya bambanta gaskiya da ƙarya, kuma ya auna hikimar duka umurni. Gā itāciyar rāyuwa mai ɗauke da ƴāƴan ɗaukakar Ubangiji Allah, maɗaukakin sarki, mai ƙudura, mai girma.
Yā kai Ahmad ! Ka shaida da cēwa, a gaskiya, shīnē Allah, kuma bābu wani Allah illa shi, sarki, mai kārēwa, mafi kwatamci, mai kōwa mai kōmi, kuma wanda Ya aīko, da sūnan Ali, ma’aikin Allah nē, wanda ya cancanta mu karɓi umarninsa gabāɗayanmu.
Ka faɗī cēwa : yā ku al’umma, ku bi umarnin da Ya bā ku cikin Bāyan, Shī wanda shīnē maɗaukaki, mai hikima. A gaskiya, shīnē sarkin manzonni, kuma littāfinsa, shīnē Umul kitābi, idan dā kuna cikin māsu iya gānēwa.
Haka dai, tun daga cikin wannan kurkukun, sūdā take rēra kira a garēku. Shīnē ya cancanta da ya mīƙā muku wannan sāƙō. Wanda ya ga dāmā, ya yi wātsi da wannan galgaɗi, kuma wanda yake sō, ya zāɓi hanyar Ubangijinsa !
Yā kū al’umma, idan kun yi wātsi da waɗannan āyōyi, tō a kan wace hujja kuka dōgara imāninku ga Ubangiji Allah subahānahu wa ta āla ? Ku fiddō ta, yā ku tāron munāfikai ! Nā rantse da wanda kē riƙe da raina cikin hannunsa, bā zā su iyā ba yau, bā zā su iyā ba gōbe, kō dā sun haɗu suna tallafar jūna, dōmin yin haka.
Yā kai Ahmad ! Kada ka manta da alhurmāta idan nā ƙaura. Ka tuna da rāyuwāta cikin rāyuwarka, da matsalōlīna, kuma da kōrar da aka mani zuwa wannan manīsancin kurkuku. Ka tsaya tsayin daka cikin ƙaunāta, kada zūciyarka ta firgita, kō dā takubban maƙiyanka zā su sassāre ka, kō kuma sama da ƙasa su kai maka hari.
Gaban maƙiyāna, ka zamana tamkar wutar garwashi, gaban masōyāna, ka zamana kōgin rāyuwar har abada, kuma kada ka shiga cikin māsu shakka. Idan bisa hanyāta, matsala tā sāme ka, kō sabōda ƙaunāta, an cī maka mutunci, kada ka dāmu.
Ka dōgara ga Allah, Ubangijinka, Ubangijin ubanninka, alhāli mutāne suna ɓata bisa hanyōyin zato, bā su iya ganin Ubangiji da idānuwansu, kō su ji muryarsa da kunnuwansu. Haka dai muka tardō su, kamar yadda kake gani. Camfinsu, yā zame musu yānā, tsakaninsu da zūciyarsu, yana rufe musu hanyar Ubangiji Allah maɗaukakin sarki.
Ka tabbata cikin zurfin zūciyarka da cēwa, wanda ya yi wātsi da wannan kyāwo, yā yi wātsi da manzonnin dauri, kuma har abadin ābāda, yā gwada fāɗin rai ga Allah Ubangiji subahānahu wata ālā.
Kafa wannan āyā cikin zūciyarka, yā kai Ahmad ! kuma ka jā ta har mutuwarka, kada ka kēɓē daga bisa hanyar umurninta. Haƙīƙa, wanda ya jā wannan āyā, Allah yā ɗauki alkawarin bā shi lādan shāhidai ɗari, kuma da izinin kyautatāwa dūniya da lāhira. Wannan alhurmā, mun bā ka ita cikin rahamarmu da karāmarmu, dōmin ka zamana cikin māsu gōdiya.
Nā rantse da Allah Ubangiji subahānahu wata ālā ! Duk tālikin dake cikin matsala, kō rūdāni, idan ya jā wannan āyā da zūciya guda, Allah nā sanyayā masa zūciyarsa, ya ƙēɓē masa azabar da yake ciki, kuma ya rabā shi da matsalōlin da suka addabē shi.
A gaskiya, shīnē mai rahama, mai jin ƙai. Gōdiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin duka dūniyōyi.
- Bahá'u'lláh