Return to BahaiPrayers.net
Facebook
Daukaka ta tabbata a garēka yā Ubangiji Allah! Ina rōƙon ka ɗaga gizāgizan cikakkiyar rahamarka, ka zubo ruwan da zai wanke zukācen bāyinka da duka dauɗar da zā ta kāre huskarsu da dūbin wajenka, dōmin dukan gabāɗayansu, su bāda gaskiya a garēka, kai da ka rāyā su, ka halicce su. Ka taimake su yā Allah! Ta wajen girman īkonka, su sāmu dāmar shiga cikin hālin da zā su iya bambanta ƙamshin turāren tufāfin wanda ka ɗaukakā da sūnanka, maɗaukaki, don su sāmu dāmar ƙaunar ka, kuma su ɗanɗana dāɗin sāduwa da kai, ta yanda, kō dā zā su sāmu duka dūkiyar da kē sama da ƙasa, bā zā su daina yabon ka ba, kō su daina ɗaukaka sūnanka.
Yā abun ƙaunāta! Wanda raina ya fi sō, ina rōƙon ka, nī bāwanka wanda yake nēman fuskarshi ta sādu da tāka, ka kāre shi da waɗanda ba su bāda gaskiya ba garēka. Ka kāre shi da sūkar māshin waɗanda suka yi wātsi da sāƙonka. Ka sā wannan bāwa, ya bi umurninka, ya ɗaukaka sūnanka, ya maida hankalinsa wajen abun da ka sauko. Hakika, kai nē wanda har abada, ba ka taɓa kōre daga ƙōfar rahamarka ba, duk waɗanda suka dōgara garēka, kuma ba ka hana duk mai nufa wajenka ba, ya iso fādar karāmarka, bā wani Allah sai kai, maɗaukakin sarki, ƙadiran mabuwāyi jalla, marar iyāka.
- Bahá'u'lláh