Return to BahaiPrayers.net   Facebook

Rānar haifuwar Bab (aminci ya tabbata a garēshi)

Da sūnan wanda aka haifa a wannan rāna, wanda Allah ya haliccē shi dōmin ya zama kākākin sūnansa mai īko, mai ƙauna.

Gā allon da muka bayyana a wannan dare da sama da ƙasa suka haskaka da hasken da ya baza ƙyalƙyalinsa bisa duk halitta.

Yā kai wannan dare ! yabo ya tabbata a garēka, sabōda daga garēka nē rānar Ubangiji Allah ta fito, rānar da cikin ƙudirinmu, zā ta zamana fitilar tsīra ga duka mazaunan birānen sūnāye, kuma da ita cē kambun nasarar zakarun dake cikin fagen fāmā na har abada, kuma da ita cē assubāhin murna da zumūɗi ga duk halitta.

Yabo matuƙa ya tabbata ga Allah Ubangiji, mahaliccin sammai, wanda ta garēshi wannan rānā ta ambaci wannan sūna, ta kēcē lābilan zatuttuka na wōfi, ta shūɗē yanannakin tunānin banza, kuma da garēta sūnansa na innanaha, ya bayyana a jiririn hakīka. Ta garēka nē aka būɗē tūlun ruwan rāyuwa har abada, aka būɗē makullin ƙōfōfin sani da na kalma ga idānuwan al’ummōmin dūniya, kuma bazarar Arrahamānu ta būsa a kōwane wajāje. Ɗaukaka ta tabbata ga wannan sā’i da cikinsa nē alfarmar Ubangiji, mai īko, masani, mai hikima ta bayyana !

Yā kē majalasar sama da ƙasa ! Wannan nē daren farkon da Allah ya sō shi da zama alāmar dare na biyu da aka haifi Wanda bābu kirārin da ya isa ya kwatanta matsayinsa. Murna ta tabbata ga wanda ya yi tunāni bisa waɗannan darāre biyu : a gaskiya zai gāne da cēwa, kasancēwarsu da ake gani tā daidaita da tūshensu na ainafi, kuma zai gāne ya fahimta da gaibunan da suke ƙunshe a cikin wannan wahayi, wahayin da ta garēshi nē ginshikan īmānin ƙarya suka rūshe, gumāken camfi suka tarwatse, kuma aka warware tūtar dake furucin cēwa « Bābu wani Allah illā Shī, mai īko, al malīku, mafi kwatanci, mai kārēwa, Al azīzu, da ya fi a kai garēshi ».

A wannan dare nē, ƙamshin turāren kusanta ya bazu, ƙōfōfin haɗuwa a rānēkun ƙarshe suka būɗe warai, kuma duk halitta ta gilgizu tana faɗa cēwa : « Daula ta Allah cē, Ubangijin duka sūnāye, shī da ya zō da mulki na musamman ya mallaki dūniya gabāɗayanta !». Wannan dare, majalasar samāniya tā karrama yabon Ubangijinta, Al’malīku, Maɗaukakin Sarki, kuma gaskiyar sunāyen Allah ta yi yabon Wanda Shīnē sarkin farkō da ƙarshe a wannan wahayi, wanda ƙarfinsa ya sā tsaunika suka zāburo zuwa wajen wanda ya isa ga kōmi da kōwa, mafi ɗaukaka, ya jūya zukācen masōya wajen fuskar masōyinsu, ya sā bazarar ƙauna ta mōtsa ganyāye, cikin murna, muryōyin itāce suka amshi kiran wanda bā shi da iyāka. Duka dūniya ta yi gilgiza cikin bēgen kaiwa ga Sarki madawwami, kuma wannan kalmā ɓōyayyā ta bayyana cikin īkon sūnā, ta maida kōmi ya zama sābo.

Yā kai daren Al’karīmu ! A gaskiya, a garēka muna ganin umul kitābi. Shin, kitābi nē, kō kuma haifaffan ɗā nē ? Āā, nī da kaina nā shaida cēwa ! waɗannan batūtuwa na daular sūnāye nē alhāli kuwa, Allah Ubangiji yā ɗaukaka wannan kitābi sama da duka sūnāye. Ta wannan kitābī nē, gaibu ɓōyeyye da ingantaccen sirri suka bayyana. Nā rantsē da rāyuwāta cēwa, duk abun da aka ambata na daular laƙani nē, alhāli umul kitābi nā sama da duk waɗannan abūbūwa. A garēshi nē alāmun « Bābu wani Allah sai Allah » suka bayyana sama ga kōmi. Nā shaida cēwa, kō da yake kōwa yā san da haka, kamar yanda Ubangijinka ya sanar, kunnansa nē kawai yake iya jin su. Murna ta tabbata ga wanɗanda suka amince da wannan !

Sai cikin māmāki, alƙalamin Mai sama ya yi kira cēwa : « Yā kai wanda kai nē ɗaukakakke sama ga duka sūnāye ! īnā rōƙon ka, don girman īkonka da ya mallaki sama da ƙasa, ka sauke mani nauyin ambatar ka, sabōda nī kaina, nā kasance don īkonka mai rāyāwa. Ta ƙāƙā zan iya kwatanta duka abūbuwan da duk halitta ta kāsa kwatantāwa ? Amā fa, nā rantse da ɗaukakarka, idan na furta ilhāmar da ka sā a raina, duk halitta gabāɗayanta, zā ta mutu don murna da jin dāɗi, abun dake nūna cēwa, a wannan haskekken wuri maɗaukaki wanda ya wuce kōmi, wannan halitta zā ta gamsu gaban tēkun kalmarka. Yā Ubangiji, ka yardēwa wannan alƙalami mai wata-wata, ya dēna kirārin wannan muhimmin matsayi, kuma ka dūbē ni da idon rahama, yā kai Sarkīna Ubangijina. Ka manta da kuskurēna a gabanka. A gaskiya kai nē Ubangijin falalā, Mai īkō, mai gāfartāwa kullun, Al’karīmu.

(Ayyan-i-Tis’ih shāfi 12 zuwa 15)

 


English  
ភាសាខ្មែរ  
አማርኛ.  
Afrikaans  
Alaska Native  
American Indian  
Azərbaycan  
Bahasa Indonesia  
Bahasa Malaysia  
Bidayuh  
Bosanski  
Canadian Indigenous  
Català  
Cebuano  
Česky  
Chamorro  
Chichewa  
Corsica  
Cymraeg  
Daga  
Dansk  
Deutsch  
Dzongkha  
Eesti  
Español  
Esperanto  
Euskara  
Fiji  
Filipino  
Føroyar  
Français  
Frysk  
Hausa  
Hawaiian  
Hiri Motu  
Hrvatski  
Irish  
Íslenska  
Italiano  
Kabyle  
Kalaallisut  
Kiribati  
Kiswahili  
Kreyol Ayisyen  
Kuanua  
Kube  
Latviešu  
Lëtzebuergesch  
Lietuvių  
Luganda  
Magyar  
Malagasy  
Malti  
Māori  
Marshallese  
Melpa  
Montenegrin  
Nalik  
Namibia  
Nederlands  
Norsk  
Papiamentu  
Polski  
Português (BR)  
România  
Sámi  
Samoan  
Sarawak  
Sesotho  
Shqip  
Slovenščina  
Slovensky  
Sranan Tongo  
Srpski српски  
Suomi  
Svenska  
Tetum  
Tiếng Việt  
Tok Pisin  
Tongan  
Türkçe  
Türkmençe  
Tuvalu  
Vanuatu  
ελληνικά  
Беларускі  
български  
Кыргыз  
Монгол хэл  
Русский  
Тоҷикӣ  
Україна  
հայերեն  
اُردُو  
العربية  
فارسی  
नेपाली  
मराठी  
हिंदी  
বাংলা  
ગુજરાતી  
ଓଡ଼ିଆ  
தமிழ்  
తెలుగు  
ಕನ್ನಡ  
മലയാളം  
ภาษาไทย  
ພາສາລາວ  
한국어  
日本語  
简体中文  
繁體中文  
Windows / Mac