Return to BahaiPrayers.net
Facebook
Rānar haifuwar Baha’u’llah (aminci ya tabbata a garēshi)
Shīnē tsarkakakke, maɗaukaki, Mafi girma
Rānar bukin karramāwa cē, wandan shīnē kyāwon Ubangiji Allah, jabbāru, mai īko, mai ƙauna, yā hau gadon īkonsa. Murnā ta tabbata ga wanda, a wannan rānā ya kai garēshi, kuma wanda Allah, mai cēto cikin matsala, madawwami, ya dūbi wajensa. Ka cē: Mun karrama wannan buki cikin kurkuku mafi girma, a lōkacin da sarākunan dūniya suka tāshi suka yāƙē mu. Ammā fa, ƙarfin azzālumai har abada bā ya iya jā da mu, kuma rundunōnin dūniya har abada bā su iya murƙushe mu. Haka Arrahamānu yake shaidāwa.
Ka cē: ashē yā cancanta a tūre tūshen hakīkantaka gaban sūrūtan al’ummōmin dūniya? Ā’ā, nā rantse da kyāwonsa dake haske duk abūbuwan dā da na gōbe! A gaskiya wannan cē alfarmar Ubangiji da take lulluɓē duk halitta, kuma haka nē īkonsa da ya mallaki duk abūbuwan dake gani da duk abūbuwan da ake gani. Ku riƙe igiyar muhimmin īkonsa, kuma ku ambaci Ubangijinku mai ƴanci, a wannan assubāhi da haske yake gwada duk gaibu ɓōyeyye. Haka nē madawwami ya faɗa a wannan rānā da aka būɗe zāɓeɓɓen ruwa. Ku yi hattara, kada tunānin shirmen waɗanda suka ƙi yarda da Allah su tāda hankulanku, kō kuma zatuttukansu na wōfi, su nīsantā ku da madaidaiciyar hanya.
Yā kē al’ummar Baha! bisa fukāfukan dangana, ki hira ki shiga cikin sararin ƙaunar Ubangijinki, mai rahama, kuma ki tāshi dōmin ki kai Ubangijinki ga nasara, kamar yanda ādanannun alluna suka ƙadarta. Kada ki yi jāyayya da kōwa cikin bāyūna. Ki mīƙā musu zāƙin tsarkakakkun kalmar Ubangiji, sabōda, da īkonta nē mutāne suke iya sāmun dāmar jūyāwa wajensa. Duk waɗanda a yau, ba su kula da Allah ba, sun ɓata cikin shāwarsu, cikin ba su mā gāne ba. Murna ta tabbata ga wanda, cikin ƙasƙanta da tawāli’u, ya jūya fuskarsa wajen assubāhin āyōyin Ubangijinsa.
Yā cancanta ka tāshi ka karantar da mutāne bisa abun da aka bayyana cikin kitābin Ubangijinsu, mai īkō, mai ƴanci.
Ka cē: ka ji tsōron Allah, kuma kada ka kula da zatūttukan wōfi da waɗanda suke tafiya bisa hanyar shakka da rishin ādalci suke faɗa. Da zuciya mai armashi, ka jūya wajen fādar Ubangijinka, mamallakin duka sūnāye. A gaskiya, zai taimakē ka da ƙarfin gaskiya. Bābu wani Allah illā Shī, mai īko, mai cikakkiyar kyauta.
Yana yiyuwa ka gaugauta zuwa ga ƙaramin tabki, alhāli gā babban tēku nan gaban idonka? Ka jūyā gabādayanka wajensa, kada ka bi sāwun kōwanne daga cikin kāfirai maƙaryata. Tsuntu madawwami nā wāƙā bisa rassun itāciyarmu ta Ubangiji. Nā rantse da Ubangiji Allah! wāƙarta guda ɗaya tak, tā isa ta shāwar da majalasar samāniya, har mā, mazaunan birānen sūnāye, kuma har mā waɗanda suke zāgayāwa, suna kēwaya gadon mulki sāfe da marēce.
Haka nē, ruwan kalmōmi yake zubōwa daga samāniyar ƙudirin Ubangijinka, mai rahama. Ku jākuɗo kusanta, yā ku al’umma, ku yi wātsi da waɗanda suke gardama ta wōfi da banza bisa āyōyin da Allah ya sauko, kuma da suka ƙi yarda da Ubangijinsu da ya zō musu ɗauke da hujja da shaida.
(Ayyam-i-Tis’ih shāfi 45-47)
- Bahá'u'lláh